1
Mar 2:17
Littafi Mai Tsarki
Da Yesu ya ji haka, ya ce musu, “Ai, lafiyayyu ba ruwansu da likita, sai dai marasa lafiya. Ba domin in kira masu adalci na zo ba, sai masu zunubi.”
Comparer
Explorer Mar 2:17
2
Mar 2:5
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu sai ya ce wa shanyayyen, “Ɗana, an gafarta maka zunubanka.”
Explorer Mar 2:5
3
Mar 2:27
Sai ya ce musu, “Ai, Asabar domin mutum aka yi ta, ba mutum aka yi domin Asabar ba.
Explorer Mar 2:27
4
Mar 2:4
Da suka kāsa kusatarsa don yawan mutane, suka buɗe rufin soron ta sama da shi. Da suka huda ƙofa kuwa, suka zura gadon da shanyayye yake kwance a kai.
Explorer Mar 2:4
5
Mar 2:10-11
Amma don ku sakankance Ɗan Mutum na da ikon gafarta zunubi a duniya” sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi ka ɗauki shimfiɗarka ka tafi gida.”
Explorer Mar 2:10-11
6
Mar 2:9
Wanne ya fi sauƙi, a ce wa shanyayyen, ‘An gafarta maka zunubanka’, ko kuwa a ce, ‘Tashi ka ɗauki shimfiɗarka ka yi tafiya’?
Explorer Mar 2:9
7
Mar 2:12
Sai ya tashi nan da nan, ya ɗauki shimfiɗarsa, ya fita a gaban idon kowa, har suka yi mamaki duka, suka ɗaukaka Allah suna cewa, “Ba mu taɓa ganin irin haka ba!”
Explorer Mar 2:12
Accueil
Bible
Plans
Vidéos