1
Mar 5:34
Littafi Mai Tsarki
Sai ya ce mata, “'Yata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya, ki warke daga cutarki.”
Compare
Explore Mar 5:34
2
Mar 5:25-26
Sai ga wata mace wadda ta shekara goma sha biyu tana zub da jini, ta kuma sha wahala da gaske a hannun masu magani da yawa, har ta ɓad da duk abin da take da shi, amma duk a banza, sai ma gaba-gaba cutar take yi.
Explore Mar 5:25-26
3
Mar 5:29
Nan take zubar jininta ta tsaya, ta kuma ji a jikinta an warkar da cutarta.
Explore Mar 5:29
4
Mar 5:41
Ya kama hannunta, ya ce mata, “Talita ƙumi”, wato, “Ke yarinya, ina ce miki, tashi.”
Explore Mar 5:41
5
Mar 5:35-36
Yana cikin magana, sai ga waɗansu daga gidan shugaban majami'a suka ce, “Ai, 'yarka ta rasu, me kuma za ka wahalar da Malamin?” Amma Yesu bai kula da abin da suka faɗa ba, ya ce wa shugaban majami'a, “kada ka ji tsoro, ka ba da gaskiya kawai.”
Explore Mar 5:35-36
6
Mar 5:8-9
Ya faɗi haka ne domin Yesu ya ce masa, “Rabu da mutumin nan, kai wannan baƙin aljan!” Yesu ya tambaye shi, “Me sunanka?” Sai ya amsa ya ce, “Sunana Tuli, don muna da yawa.”
Explore Mar 5:8-9
Home
Bible
გეგმები
ვიდეოები