1
Mat 27:46
Littafi Mai Tsarki
Wajen ƙarfe uku kuma sai Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Eloi, Eloi, lama sabaktāni?” Wato, “Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni?”
Comparer
Explorer Mat 27:46
2
Mat 27:51-52
Sai labulen da yake cikin Haikalin ya tsage gida biyu, daga sama har ƙasa. Ƙasa ta yi girgiza, duwatsu kuma suka tsattsage. Aka bubbuɗe kaburbura, tsarkaka da yawa da suke barci kuma suka tashi.
Explorer Mat 27:51-52
3
Mat 27:50
Sai Yesu ya sāke ɗaga murya da ƙarfi, sa'an nan ya săki ransa.
Explorer Mat 27:50
4
Mat 27:54
Sa'ad da jarumin da waɗanda suke tare da shi suna tsaron Yesu suka ga rawar ƙasa da kuma abin da ya auku, sai duk tsoro ya kama su, suka ce, “Hakika wannan Ɗan Allah ne!”
Explorer Mat 27:54
5
Mat 27:45
To, tun daga tsakar rana, duhu ya rufe ƙasa duka, har zuwa ƙarfe uku na yamma.
Explorer Mat 27:45
6
Mat 27:22-23
Bilatus ya ce musu, “To, ƙaƙa zan yi da Yesu da ake kira Almasihu?” Duk sai suka ce, “A gicciye shi!” Ya ce, “Ta wane halin? Wane mugun abu ya yi?” Amma su sai ƙara ɗaga murya suke ta yi, suna cewa, “A gicciye shi!”
Explorer Mat 27:22-23
Accueil
Bible
Plans
Vidéos