1
Mar 2:17
Littafi Mai Tsarki
Da Yesu ya ji haka, ya ce musu, “Ai, lafiyayyu ba ruwansu da likita, sai dai marasa lafiya. Ba domin in kira masu adalci na zo ba, sai masu zunubi.”
Compare
Explore Mar 2:17
2
Mar 2:5
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu sai ya ce wa shanyayyen, “Ɗana, an gafarta maka zunubanka.”
Explore Mar 2:5
3
Mar 2:27
Sai ya ce musu, “Ai, Asabar domin mutum aka yi ta, ba mutum aka yi domin Asabar ba.
Explore Mar 2:27
4
Mar 2:4
Da suka kāsa kusatarsa don yawan mutane, suka buɗe rufin soron ta sama da shi. Da suka huda ƙofa kuwa, suka zura gadon da shanyayye yake kwance a kai.
Explore Mar 2:4
5
Mar 2:10-11
Amma don ku sakankance Ɗan Mutum na da ikon gafarta zunubi a duniya” sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi ka ɗauki shimfiɗarka ka tafi gida.”
Explore Mar 2:10-11
6
Mar 2:9
Wanne ya fi sauƙi, a ce wa shanyayyen, ‘An gafarta maka zunubanka’, ko kuwa a ce, ‘Tashi ka ɗauki shimfiɗarka ka yi tafiya’?
Explore Mar 2:9
7
Mar 2:12
Sai ya tashi nan da nan, ya ɗauki shimfiɗarsa, ya fita a gaban idon kowa, har suka yi mamaki duka, suka ɗaukaka Allah suna cewa, “Ba mu taɓa ganin irin haka ba!”
Explore Mar 2:12
Home
Bible
Plans
Videos